Thursday 30 August 2018

Wakar "Ranar Kilishi Jikar Dikko" ta Mamman Shata Katsina


Wannan waka, mai amshin "Ranar Kilishi Jikar Dikko", Mamman Shata ya rera ta ne ga Hajiya Kilishi, matar Sarkin Daura Muhammadu Bashar (Allah ya jikan shi). Jigon wakar shi ne kambamawa da yabo. A wakar, Shata ya tuno da yadda aka yi bikin auren Kilishi (diyar Sarkin Katsina Usman Nagogo) da Bashar lokacin ya na Wamban Daura.

Wannan wakar, gajera ce, to amma ta kunshi abubuwa da yawa. 1. Ta nuna cewa sarakuna a kasar Hausa na auratayya tsakanin su; 2. ta nuna kasaitar wannan bikin aure, wato irin babban taron da aka yi na jama'a da motoci da babura da kekuna, da kuma yadda sarakai ke yin babbar kyauta ga maroka ko mawakan su; 3. ta taskace mana tarihin al'adar "durbar" da Turawa su ka kawo mana, wato hawan dawakai domin nuna al'adun mu; 5. wakar ta bada tarihin ita Kilishi a takaice, wato Shata ya nuna mana cewa ita 'yar Sarki ce jikar Sarki; 6. a wakar akwai nason addinin Musulunci, musamman bangaren karatu da kuma tarihi. Misali, mun fahimci cewa Shata ya san wani abu game da wasu wakokin Larabci, wato irin "Alburda", da mawakan Larabci irin su Alfazazi.
Na rubuta wakar ne daga wani faifan Shata da na saurara.
Na alamta inda aka yi amshi da alamar tauraro, wato *. Bismilla.


SHATA: Ranar Kilishi jikar Dikko.

AMSHI (*)

Ranar Kilishi jikar Dikko.
*
Bukin Kilishi jikar Dikko,
Taron ta sai ka ce an Durbar:
Mota dubu ta je tarbar ta,
Doki dubu ya je tarbar ta,
Dike dubu ya je tarbar ta,
Ba sa'ikul ba, ba 'yan ƙas ba,
Tarbar Kilishi jikar Dikko.
*
Rad da Wamban Daura jikan Abdu,
Mamman jikan Sarki Musa,
Jikan Muska da Sarkin Fada,
Jikan Muska da Sarkin Fada,
Ran nan Wambai yab ban mota,
Yac ce don darajar ɗan Hamza,
Sardo Amadu jikan Shehu,
Sai ko Kilishi ta ce ita ta ba ni domin Amadu jikan Shehu.
*
Daidai, Kilishi jikar Dikko!
*
Kilishi Allah ya ba ki ladan aure,
Da ma ki san gidan Aljanna.
*
Da sauya waƙar Kilishi jikar Dikko,
Yara su na ta dukan fata,
Kiɗan sai ka ce fitah harsashi!
*
Zuba waƙa ni kai,
Ni sai zuba waƙa ni kai kama da ta Alfazazi,
Kamar ana tamsiri.
*
Zuba waƙa ni kai kama da ta Alfazazi,
Kamar ana Alburda.
*
Ta Tatsumburum garin Ɗanyaro,
Waccan Kilishi jikar Mamman,
Waccan Kilishi jikar Mamman,
Wannan Kilishi birnin Dikko,
Wannan Kilishi birnin Dikko,
Kakan ta Shehu ne Usumanu,
Baban ta Shehu ne Usumanu,
Kakan ta kau Muhamman Dikko.
*
Kilishi kakan ta kau Muhamman Dikko.

*
Kilishi kakan ta kau Muhamman Dikko.
*
Allah ya ba ki ladar aure,
Da ma ki san gidan Aljanna.
*
Daidai, Kilishi jikar Dikko.
*
Taron Daura ya kai taro,
Taron Daura ya kai taro,
Bukin Kilishi jikar Dikko.

Farashi da inda za a samu "Shata Ikon Allah!"



Daga gobe Juma'a idan Allah ya kai mu za a samu wannan littafin na "Shata Ikon Allah!" wasu wurare a arewacin kasar nan. Za mu ci gaba da fadada wuraren. A yanzu dai ga inda za a same shi:

Abuja: Shagalinku Restaurant da Sahad (Main)
Kaduna: Arewa House Bookshop da Hamdala Hotel Bookshop
Kano: Sahad Supermarket, Zoo Road
Katsina: Matasa Media Links, K/Kaura

KO A KIRA WADANNAN LAMBOBIN:

Kaduna: Abba - 08069518667;    Joke - 07030489082
Kano:     Abubakar - 07061838558;   Mukhtar - 07030924846
Abuja:   Ashafa - 08056363602;  Yahaya - 08039727242
Katsina: Danjuma - 08035904408;    Umar - 08037549033

KO A TUNTUBE MU TA NAN:

WhatsApp: 08036890400; 08141565625
 
Facebook: Shata Ikon Allah (group)

Instagram: Mamman­­_Shata

FARASHI:

Softcover: N8,000

Hardcover: N10,000

Wednesday 29 August 2018

Littafin "Shata Ikon Allah!" ya fito!

Littafin "Shata Ikon Allah!"



Alhamdu lillah! Alhamdu lillah! Alhamdu lillah!

Bayan na shafe shekara 12 ina aiki kan sake rubuta shahararren littafin nan na tarihin Alhaji (Dr) Mamman Shata Katsina, da zurfafa bincike a kan rayuwar sa, a yau dai Allah (SWT), mai kowa mai komai, ya yi ikon sa, littafi ya shigo hannu na. An kammala dab'in sa da shirya shi a bisa sabon fasalin da ya dauka. Allah na gode maka!

Wannan littafi, wanda Shata da kan shi ne ya ba ni izinin rubuta shi, ya bambanta da wanda na jagoranci rubutawa a baya, wato wanda ya fito a shekarar 2006. Ko makaho ya shafa, zai ji bambancin. Ya inganta ta fuskar kyautata bincike da nazari, ya inganta ta fuskar yawan shafuka, ya inganta ta fuskar kyan dab'i, ya inganta ta wajen yawan shafuka.

Shafi 921 ne. Akwai shafi 32 masu dauke da hotuna masu kala, wadanda aka buga kan takarda mai santsi.

A cikin littafin, akwai hotuna guda 580. A cikin su, akwai hotuna masu kala har 98.

Babu littafin da na taba shan wuyar rubutawa kamar wannan. Na yi yawo a garuruwa da kauyuka. Na kashe kudi ban san adadin su ba. Na rika zama a tebur, a gaban komfuta, daga safe zuwa karfe 2 na dare, na tsawon watanni, na hana kai na more rayuwa yadda ya kamata, kafin wannan aiki ya kammala. Sannan na sha fama da masu cewa don Allah yaushe wannan littafi zai fito? Masoyan kenan. Na sha fama da masu zunden cewa na rike littafi, na hana shi fitowa. To, Allah ya yi - wai aure da mara kwabo - a yau ga kwafen littafin ya shigo hannu na.

To yaushe zai shiga kasuwa? Ai har ma ya shiga, domin kuwa ko a gobe za mu iya sayar da shi ga duk mai so.

Addu'a ta ita ce Allah ya sa a ce gara da aka yi. Allah ya sa albarka.
Allah ya jikan Alhaji Muhammadu Shata, amin.


Ibrahim Sheme

Sunday 26 August 2018

Waƙar "Taimaka Rabbana" ta Sani Sabulu Kanoma

Baitikan da na fi so a waƙoƙin Alhaji Sani Sabulu Kanoma su na cikin waƙar sa ta "Taimaka Rabbana". Ga su na zauna na rubuta su kamar haka:


In ka na yawo cikin duniya,
Kag ga abin mamaki bai kamar ƙarewa,
Sai kullum ƙaruwa za ya yi.

Sai ka samu mutum cikakken mutum,
Ka iske mutum kamak kamili,
Hannu na mutum, idanun mutum,
In ka koma cikin zuciya tasa sai ka ga ƙwamma kura da shi!

Ka san sha'anin duniya wuya ce garai,
In an ka iya shi daɗi garai.

In kay yi kure, akwai 'yaw wuya.

Ya ikon Allah, ka tserad da mu ka hana mu faɗa ka ganar da mu gaskiya.

Taimaka Rabbana, ya Jallah ka ceci 'yan zamani.

Ka san sha'anin duniyag ga sai Rabbana.

Ka san sha'anin duniya wuya ag garai,
In ka ga mutum ka na ra'ayi nai malam,
Kafin ku zam jiki kai da shi, na so ka yi bincike nai kaɗan,
Ka bar dubin fuska da kaurin jiki,
Na so ka yi binciken zuciya da irin halin da duk ag garai.

Ka san cinikin ɗan'adam wuya ag garai,
Ko an bar ma sule goma nan a cikin naira rage sule biyar,
Watakila ka na zaton faɗuwa.

Ka san hikima - eh?
Sha'anin duniya wuya ag garai.
Amma inji mai waƙa uban Zainaba, Sani,
Amma inji mai waƙa uban A'isha, Sani.

Sha'anin duniya wuya ag garai,
Sannan cinikin ɗan'adam wuya ag garai,
In an ka biyo ana bincike, ka je ka hwaɗi garan an ka ji.

Taimaka Rabbana, ya Jallah ka ceci 'yan zamani.
Ya ikon Allah, ka tserad da mu ka hana mu faɗa ka ganar da mu gaskiya.
Ka san sha'anin duniyag ga sai Rabbana.

Ka samu mutum cikakken mutum,
Hannu na mutum, idanun mutum, a'ah!
Daidai ya yi godiyar Rabbana, sai ka iske ana ta'asa da shi.

Allah ya yi ma jiki na mutum,
Kuma yai maka lafiya ta mutum,
Daidai ka yi godiyar Rabbana, sai ka iske ana ta'adi da kai.

Ka san sha'anin duniyag ga sai Rabbana.

Ka samu mutum kamar kamili,
Ka iske mutum cikakken mutum, (2x)
Ga riga, cikin rawani,
Da ka koma cikin zuciya tasa sai ka ga ƙwamma kura da shi!

Ka san sha'anin duniyag ga sai Rabbana. (2x)

Thursday 23 August 2018

Garba Dangida at 62: A Short Appreciation

Alhaji Garba A. Dangida in his office - in those days!
Here is a special Happy Birthday greeting from me to a man I respect so much. Alhaji Garba Dangida, the publisher of Abuja Newsweek magazine, clocked 62 yesterday. May the almighty God continue to give him good health, wealth and, above, all rest of mind, amen.

We first met in 1991 when I was the Deputy Editor of a Kaduna-based weekly newspaper, Nasiha, the Hausa language sister of the daily newspaper The Reporter, both published by the late General Shehu Musa Yar'Adua. Alhaji Garba was at the time the publisher of Katsina Newsweek, the first indigenous newspaper established in my state (it became Abuja Newsweek when he moved to Abuja). He had gone to the newspaper company where I worked in order to print his magazine when we met and, I guess, we clicked almost immediately.

From then on, as I waded through life, working here and there as a journalist, I served in various capacities (though without any appointment letter!) as Alhaji Dangida's newspaper and magazine Editor, his P.A., S.A., Senior Special Adviser, errand boy, confidant, business partner, younger brother, co-conspirator, son, etc. Sometimes I combined two or more of those roles.

Through it all, I saw in him a special breed of human being: kind, selfless, loyal, humorous, jovial, fun-seeking, philanthropic, diplomatic and patriotic. He also has a way with business which I can simply describe as a Midas touch, i.e. whatever he touched turned to gold. I reckon he acquired that acumen during his long stay in Lagos where he worked with some expatriate businessmen. He is simply a goal-getter. Surely, he has his own downsides, like us mortals, but those have been outweighed by the positives that he exudes.

Even know he didn't know it, I actually learnt many lessons from him about business, family life, relationship with friends and foes alike, and just what it takes to survive in the shark-infested waters of Nigerian life. One of those great lessons is that you must have the heart to forgive those who hurt you and accommodate those whose views or perspectives contradict yours. Another lesson is that you must go out of your way to be kind. Another lesson is that you must strive to be friends with your kids. Another lesson is that the daggers of backbiters may hurt, but they cannot fierce through the focused heart. Yet another lesson is that you must respect people, not only those of your own tribe or religion but also those of different backgrounds. And whilst you seek pleasure and joy, it must not bother you that you aren't as rich as the other fellow.

As Alhaji Dangida piles on the years, I noticed that he has not lost his well-known penchant for gracefulness, looking good and speaking wisely. Sadly, however, I also noticed that he and I hardly meet even though we live in the same city; we speak on the phone occasionally, but generally we were closer when we lived in different cities! Why? Search me.

Alhaji Garba Dangida may not be as materially rich as some might think, but I see him as I always regarded him from the very first time of our acquaintance - a rich, fulfilled man. He lives well by the  standard I personally set for one to be living well. And he is an achiever in business, family life and human relations.

My prayer for him as he quietly celebrates the unique milestone of his birthday is to continue to savour his achievement in the three areas I described above - and eternally enjoy God's grace in this life and the next. Amen.